logo

HausaNovel: Aure Kan Aure! (4)


Aure kan Aure
Chapter4


Tunda suka hau hanyar qauyen naafisa ta dinga
waige waige Can dai ta kasa daurewa ta dubeshi
tace Tace kai aleeyu wai yanxu mutanene ke
rayuwa a Cikin wannan dajin kauyen?
Tambayar tata ta bigi zuciyarsa tazo masa wuya
Yai wata murmushi da za* a iya kira da yaqe
yace
A wannan dajin kauyen da kika gani mahaifinki
yai rayuwa tun yana dan shekara sha biyar har
yakai ashirin
Tsit tai tankar ruwa ya cita amsar tai mataqar
yima kausar dadi
Dan ko banza yayi maganin iskancinta
A qofar Gidan nasu direba yai parkin suka sauka
nafisa sai bin lungun Gidan nasu da kallo take
Yai gaba yana kuzo mu shiga yai gaba suka
biyoshi a baya
Ba laifi Gidan shafaffene da siminti da hanzarinta
innan tasa ta taSo tana sannunku da zuwa
maraba da
Manyan baqi
Ku shiga daga ciki
Kowa ya cire takalminsa amman nafi taqi da nata
ta shiga
Dakin sai kamshi yake ga saitin kujeru
Kausar ta zauna daga qasa nafi kuwa ta dare kan
kujera ta daura qafa daya kan daya sai kadasu
take tana taunan cingam
Aleeyu bai shigoba dan yana waje suna magana
da inner tasa
Kausar ta yafitota murya qasaqasa tace dan Allah
sauke qafafunnan naki anty ki cire shoes dinnan
babu dadi wlh
Taja wani gajeran tsaki tana fadar har Wasu
tsofaffin kirkine da zan
Guji bacin ransu
A wace tashar ake nunosu ko a wace jaridar ake
bugasu?
Ta qarajan wani dogon tsaki tana
Kada ki kuma batamin rai
Bata sake magana ba Sbd tahowar innar
Baqi hansha hanya ya aka baro iyayen?
Duk kausar ne ke amsa Mata sannan direba ya
gaisheta
Saida suka Gama gaisawane sannan nafi tace ina
yini?
Lfy lau ta amsa tana tambayarta ya hanya
Inna ta dubi Direban tana wacece sirikar tamu?
Yai murmushi ya nuna Mata nafi sai taga makar
kausar ya nuna Mata dan haka fara!ar tata ya
qaru
Dan ta yaba da natsuwar kausar din
Inna ta miqe ta kawo musu burabuskon alkama
Wanda tai musu da miyar kaji
Abinci sai qamshi yake aleeeyu ya kawo musu
lemuka da robar ruwan swan
Sannan yacema Direban da ya taso suje suci
nasu a can Dakin tsohon nasa
Kausar ta dubita tace sauko mu dan taba abinnan
kar muqici ba zasuji dadiba
Da wata harara ta bita tace nice zzanci wannan
abincin?wato kwalara ta kamani ko?
To bazanciba in sunxo sun iske bamuciba haushi
e kashe su
Bata sake maganaba kausar din ta sauka ta zari
flate ta zuba burabuskon dadin abin ya ratsata
nanfa ta zauna ta cika cikinta
Da suka Gama inna ta shigo domin tattara kayan Kausar tace barshi dan Allah mama bari zan
tattara
Inna tace kekam barshi dan Allah yarnan keda
kukaxo baqunta
Tsalam sukaji murya nafi na fadin kekam ki
barshi ta kwashe mana
Kinfa cika naci Kamar tsohuwa
Kausar taji kalaman nafin tamkar saukan ruwan
zafi tace a,a inna barshi
Barshi ai nayau ne kawai
Dan haka ta kyaketa
Ta tattara taje ta wankesu tas
Bayan ta Gama ta nufi Dakin nafi ta bita da
harara tana fadin to ayawo
Ina kikaje a wannan garin me kama da bola?
Bata tanka musu ba Sbd inna na Dakin kausar ta
qosa su
Tafi Sbd yaddah nafi keta kwabasa musu kartai
abinda zatasa a zagi iyayensu
Tai sa,a kuwa aleeyun ya shiga yace kuxo mu
gaishe da malam gashinan ya shigo saimu wuce
Kar muyi dare a hanya inna tace a,a su bari ko
sallah sayi ko?
Basuce komaiba suka wuce kausar ta duqa har
qasa tana gaida malam
Nagartaccen dattijo
Nafi ta qare masa kallo tace a xuciyarta ashe
aleeyu shi ya biyo kyakkyawan dattijo
Tamkar shi e kansa
Ya maida hankalinsa kan kausar dan yayi zaton
ko Itace sirikar tasu
Nan yai musu addu,a sannan kausar tai sallah
Bayan sun kimtsa aleeyu yasa direba ya shigo
musu da tsaraba sannan Sukai sallama
Suna kan hanyane kausar ta dubi aleeyu tace
Kai yaya aleeyu ashema garin nake ba wani
kauye bane sosai aini ina sha,awar irin wannan
garin
Da ace nan zaku zauna da babu abinda zai hana
na dinga zuwa muku hutu
Ji Sukai tace kan abinda malam ya hana ta ta
kundumo Mata wata
Ashar tana fadin kausar me kika maidanine?
Kina nufin a kawoni wannan takurarren garin
Ammman baki qaunata duk garinnan ina kika ga
yai miki kama da inda za,a sakani?
Allahi ya kyauta nai rayuwa cikin gidadawa yan
kauye jahilai
Karki sake maimaitamin wannan kalaman
Inba so kike ranki ya baciba dan nida garinnan
har abada
Shiru kausar tayi dan abin yamafi qarfin tunaninta
Shikuwa aleeyu takaicine ya Gama kumeshi ji
yake tamkar ya maqureta ya huta
Yace Aransa anya tasu zatozo daya kuwa
Ansha biki amarya ta tare a katafaren gidanta
Lokacinda iyayen aleeyu sukaji ba kausar bace
amaryar abin bai musu dadiba saidai babu
yaddah suka iya
Rainin hankalin nafi sai qara gaba yake sam bata
ganin mtuncin iyayensa
Da danginsa ko kadan shiyasa yanxu dangin nasa
baSu cika kawo masa
Ziyara ba
Tunda akai auren shekara biyu kenan bata taba
zuwa gaishe da iyayensa ba
Yayi nacin har ya gaji
Yan,uwa har an fara yi dasu jowa yasan baiyi
sa,ar mataaba
Daya samu lbrn iri wulaqancin da takema
danginsane
Yaxo yai Mata tatasa shinefa yanxu idan sunxo
take barinsu suna shiga Gidan ammanfa zasuga
wulaqanci hardana bugawa a jarida
Ya Bude idanunsa wandanda suka rine tamkar
garwashin wuta
Ina amfanin rayuwa da macen da batasan darajar
iyayen
Mijinta da danginsa ba da wadannan tunane
tunanen har Barci ya kwashesa
Saida aka kira
Sallar asuba sannan ya samu damar miqewa yai sallah sannan ya fara shirin tafiya office a sashin
saukar baqi ya samu kwaggon nasa inda yake
musu bayanin yanxu
Zai hadasu da direba Wanda zai kaisu kasuwa ya
siyo musu duk abubuwan da suke buqata
daganan ya kaisu tasha
Su hau mota daganan ya ciro kudi masu yawa ya
miqama kwaggon yace ga wannan kui kudin mota
da tsaraba sannan ku riqe Wasu a wajenku
Godia suka dinga masa kwaggo harda kwallan
farinciki
Sannan yai musu sallamaa ya wuce office din
nasa
Misalin qarfe goma na safe nafi ta farka daga
barcin da take
Kai tsaye toilet ta nufa ta watsa ruwa sannan
tayo qasa domin yin break
Bayan ta zaunane take kwalama ladidi kira da
saurinta ta qaraso tana gani hajia
Tace
Meye da meye anan?
Ta fara lissafa Mata tadan yamutsa fuska kamin
tace zubamin dankalin
Ad sandwich a gefe
Ta amsa da to
Bayan ta Gama ta fice Kamar daga sama taji ana
knocking
Tace hu is knocking
Sorry sweety taji an fada ta miqe da sauri tana
fadar
Am coming my dear
Ta meqe da sauri ta Bude Dakin tana budewa
suka maqale juna tana fadin am
Sorry sury
Amman fa nayi matuqar farin cikin ganinki
Tana fadin sury Wlh yanxu shawarar tafiya
gidanki nnake dan
Nayi mising dinki Wlh ki yarda dani
Surayyah ta zame hannunta tana fadar ke ni rabu
dani mayaudariya kawai
Wlh afi baki sona dole na Nemo mai debemin
kewa
Mata da yawa sunamin tallar kanki ammman naqi
nace dole saike wai don kawai kar naci amanarki
Amman ke ko a jikinki
Nafi tace ba haka bae hajiya surayyah kin ganene
mijin nawane bai barina ina
Hutawa
Wata harara ta watsa Mata tace sannu mai miji
Aini kaina da nawa mijin nake wannan harkar
Bama miji dayaba
Bari na fada miki wani sirri ba miji daya gareniba
ni matar
Soja ce kuma matar chirman
Nafi tace ban ganneba sury fahimtar dani
Saida taja wani dogon murmushi kamin tace tun
daman can asalina yar qarin bauchi ce
Acan iyayena da kakan Nina suke
Ni kadai iyayena suka haifa kuma suka gani
inngattacciyar tarbiyar Arabi data boko
Bayan na Gama digirinane na hadu da wani Soja
mai suna auwal
Soyyah ta shiga tsakanina dashi har manya
sukasan da zancen aka daura mana aure
Kwatsam aka canjama auwal aiki zuwa qasar
inugu
Ni kuma na nace sai na bishi can
Shekararmu daya acam daganan aka turamu
Lagos wani qauye
Anan muka zauna na saba da mutane harkar
duniyata kawai nasa a gaba
Ke har maza nnake kawowa Gidan nawa Garine
da ba ruwan Kowa da kowa
Kwatsam rannan aka tura mai gidana wani cose a
qasar amurka Na shekara biyu ya shirya yai tafiyarsa
Ban damuba dan inada masu debemin kewa
A haka na hadu da manyan mutane can gida
kuwa babu masu ziyartata dan nayi nisa
Saidai idan nine ke keson ganinsu naje na hada
musu sha tara na arziqi
A haka na hadu da wani dan siyasa mai rike da
muqamin charman
Na lokal government dan asalin garin kano ne
Saidai shi bada watsewa ya nemeniba dan duk a
zatonsa ni budurwace
A haka ya nuna yanasona da aure na amince na
nuna masa nida
Mahaifiyatace kawai a gidanmu
Yasa ranar da zaixo ya gaisheta
Muka hada baki nida matar da nake haya a Gidan
nata
Na tsara Mata yaddah nakeson abin ya kasance
ta amince
Kabir umar yazo shida abokansa suka gaishe da
matar a matsayinta na mahaifiyata Suka bata
maqudan kudi
Muka hada baki da wani dattijo Akan ya
tsayamin a matsayin qanin mahaifina ya amince
na biyasa aka dauramin aure da wannan charman
din aka dauko
Amarya surayyah aka kawo garin kano
Shekara uku kenan da aurena da chirman ina
zuwa akai akai ina gaida iyayena
Shima Alhaji yana zuwa gaishe da wannan matar
data tsayamin a matsayin uwata
Shi kuwa mijina auwal. Soja mijina na farko har
yau bai dawoba saidai
Duk qarshen wata ya turomin da. Rabin
albashinsa ni kuma naita wadaqata
Yaddah nakeso
Dan yanxu sai muyi wata bamuyi wayaba
Yar iskaceni?
Da yanxu inacan a jibge ina jiran gawar shanu
Dawowa ba rana ba lokaci
Nafi ta jinjina kai tace lallai surayyah kin cika
gawurtaCciyar yar duniya
Aure kan aurefa kenan kikai?''
Tace so wat inban morema duniyataba yanxu
hajiya Nafi to sai yaushe
Zan more
Gani yanxu ina hawa manyan motoci
Na mallaki manyan gidaje ina shga manyan store
na ratsa contry din danaga dama
Sannan ina tare da manyan yan gwamnati
Inda bani dasu koke ba zaki yarda na rabekiba
Cikin satinnan na lunco manya manyan jeef
baqaqe guda uku
Da wata. Shantaleleliya fara da naga akaimin
odersu gada ingland
Na zuba escot har sha shida ina tafe ana min
jiniya duk inda na shiga girmamani
Ake
Nafi tace kai dan Allah hajiya surayyah meye
sirrin fadamin naji?
Sani hanya yar uwa
Sury ta riqe baki tace waceni da daura zanin uwar
miji
Ai ina tabbatar miki da bazaki iyaba mumabar
wannan zancen kawai
Nafi tace haba hajiya Sury kinsan babu harjar
bakin ciki tsakaninmu
Fadamin ko meye Wlh zan iya
Inhar zan samu dukiya na tara na sai manyan
motocin da duk inda na gifta zan dinga jamyo
hankalin jama,a
Kowa ya rinqa girmamani
Sury ta dafa kafadarta tana kin samu yar uwa
inhar zaki iya
Ni kuma zan kaiki har bakin rigiyar da zaki dinga
zabaro kudi
Zaki zama miloniya Cikin kwana daya
Ta maqalqale surayyah tana fadar
Na gode aminiyata dan Allah fadamin ta wacce
hanyace
Sury ta girgiza kai tace kwantar da hankalinki
bazan tonama kaina
Asiriba kizo ki watsa min qasa a idoba
Kice ba zaki iyaba
Kwara na kaiki gindin abin yaddah baki isa ki
kubce ba
Wata yar dariya ta sake sakawa ta qara rungume
surayyar
Suka fara aikata masha,ar tasu
Daga qarshema miqewa Sukai suka haura sama
dan faga inda suke yan aiki na iya
Giftawa su kansu a kowane irin lokaci
Sai Bayan sallar issha,i Sannan suka rabu da
niyyar gobe zataxo ta dauketa dan kaita inda
rijiyar kudin nasu take
Cikin farin ciki Nafi take danji take tamkar tayi
kudinma tagana
Dan harta fara hangi kanta Cikin manyan motoci
Kekekekekekekekekekekekekekek duniya ina zaki
damu
Hm lol. Nafi dai toh badai zance komai ba.

Muhadu a chapter (5)......

Tags

advertisement centil

This blog is created for your interest and in our interest as well as a website and social media sharing info Interest and Other Entertainment.