AURE KAN AURE
'Chapter 3'
Tace bari muje gida sai ai tsada na biya
Bata jira amsarsa ba ta suri qatuwar jakan tata
ta hannu tai gaba shi kuma ya shuru akwatinan
ya saka a Cikin boot din motar ya shiga
mazaunin direba
Abin ya bashi mamaki ganin ta shiga Gidan gaba
ta zauna
Ita daya cancanci ta zauna Gidan baya ya bita
Yadan saci kallonta akai rashin sa,a itama kallon
nashi take
Ta kashe masa ido daya da sauri ya janye fuskar
tashi yasama motar key ya
Zungureta sukai gaba
Da hannu daya yake tukin ya daura daya hannun
nasa inda
Aka tanada dan daurawa ganin haka yasa tai
saurin riQo. Hannun nasa yai saurin
Waigowa tace
I like to se ur face please
Sauri yai ya maida kallonsa kan titin inda Allah
ya kiyayye da ya daki bayan wata
Babban mota yace ya Salam ganin haka ya
tattaro natsuwarsa ya daura Akan titin
Suna isa gida ya Bude. Qofa yana qoqarin fita ta
riqo hannunsa
Cikin bacin rai ya waigo ganinyanda taga fuskar
tashi
Ta canja yasa ta sakeshi tana wani
Ni,im taccen murmushi ba tare da ya qara
waigowa ya kalletaba yai gaba abinsa
Yan gidanne suka fito anata murna ga anty nafisa
ga anty nafisa
Kowa sai murna yake shi kuwa wani takaicine ya
isheshi yace shin daman
Haka Mata birni suke kodan baya hulda dasune ko a qauye shi yasa
Bai fahimci hakanba
Yace kai ina Mata wasu ababene masu natsuwa
kawaici da kunya
To ya akai ita nafisa bata da ko daya to ya akai
kausar keda duk wadannan
Abubuwan amsar da e kasa ba kansa kenan
Ya shiga sashin momyn nasu ya Bama yar aikinta
makullun zai fice kenan ta fito tace ina yar
momyn takene aleeyu yai murmushi yace gasu
can a waje hajia
Sukai wajen tare tana hango momyn nata ta sasa
ihu tai kanta ta rungumeta sai murna suke shi
kuwa kai yasa ya raba. Zai wuce
Sai ji yai kausar na fadin yaya aleeyu kai yaya
aleeyu cewa fa kai na
Hada Maka zaka dawo kaci yai murmushi yana
kallon kyakkyawan
Sanyin yarinyar na tafiyar masa da hankali
Ya waigo yana mrmushi
Yace am sory kausae mancewa nai muje
Da murnanta suka jera dinning din kichiin ta
kaishi ta xuba masa komai
Sannan taja kujera ta zauna sai hira mai dadi
taake masa
Harya gamacin abincin aamman hirar bataa
qarebaa
Kamr an jefota ta fado kichin din
Da kaallo duk suka bita yaddah taai wani kichin
kichin zaakasha waani abun bacin ran ta gaani
Fuskar kausar dauke da murmushi tace me
kikesone anty ta
Qara hade rai tace me kike anan?
Tambayar bataima kausar dadiba dan haka ta
rasaa amsar da zata bata
Da hannu tai Mata nuni da tashi ki wuce kalaman
nata suka karya Mata
Zuciya idanuwanta suka ciko da hawaye muryarta
a sanyaye tace haba anty mae
Yasa........
Ta. Katseta ise get out jiki lakwas ta miqe ta kalli
yaya aleeeyum sannan ta gaba
Har Cikin ransa. Baiji dadiba takaicine fal a
zuciyarsa
Nai ankaraba saiji yai an dafa kafadara ya waigo
da sauri ransa a bace
Cikin kakkausar murya yace meye haka nafisa ya
kike abu kamar ba musulma ba?
Itama ta zaro idanunta tace yadai kake abu
kamar ba wayayyeba
Tace haba aleeyu dubekafa namiji har namiji babu inda Allah ya tauyeka
Gaka dakyau kamar dawisu
Ga kwarjini kamar daamisa tunda nake ban tabaa
ganin namijin da zuciyata
Ta kwadaitu dashiba sai kai
Sonka nake aleeyu Wlh Sonka nake inada kishi
ban yarda ko qannena na dingaa ganin suna
kusaantarka ba ballantaana har hira ta shiga
tsakaninku
Daaan zan iyaa batawaa da Kowa akanka
Ji yai wata xufa na karyo masa Cikin hanzari ya
fice daga kichin din
Yai murmushi tace ya rage naka
Ta. Duqa ta dauki kofin da yasha juice din a ciki
ta lashe tas
Lol. Kunji mayyah
Abin duniya ya ishi kausar dan tabbas ta karanto
wani abu a idanun
Yayar tata to ya kenan?
Tace tunda take bata taba ganin Wanda lokaci
guda ta kamu da sonsa ba
Wanda ta taBbatar Shima yana son nata
Dan sau rari idan suna hira yana Mata wasu
kalamai
Dake kama Dana soyayyah tace tabbas idan
batasan abinyiba yayarta zata mataa
Shigaar saauri
Gidan Alhaji muftahu gidane dake cike da tarbiya
matarsa daya da
Yayaansa biya
Nafisa babba kausar me bi Mata
Sai ammar yusuf da kalifanafisa ta Gama digiri
dinta a wannan shekarar sai kuma kausar dake
level2. A. @B,u,k dake kano
Duk cikinsu nafisace kawai ta fita zakkah bataji
ko kadan. Dan har a dangi ana kuka da ita
Gashi ta liqema kamilin mutum irin aleeyu Wanda
kyale kyalen duniya bai
Gabansa to ya kenan?
Muje zuwa
Kwata Kwata aleeyu ya fitar harkaar Gidan sbd
shu,uma nafisaa
Dan ko Alhaji ya aikeshi Gidan sai yai saurin
kawo mishi uzuri
Abin ya fara damun kausar harta fara tunanin ko
yai fushi da abinda nafisa
Tai masa ne
Dan haka ta yanke hukuncin kiransa a waya
domin ta bashi haquri da sauri ta nufi dakintaa
ringin daya biyu ya dauka da fara,arta tace yaya
aleeyu ai mana afuwa tuba muke idan har laifi
mukai
Idan har laifi mukai da aka yanke mana wannan hukuncin
Yai murmushi yace waneni kausar ba abinda
kukai min
Taace to shine ka yaadamu yau sati daya kenan
baka zoba dan ko daddy bai aikokoba kaana
zuwa duba momy duk ran juma,a
Yace tuba nake ranki e Dade inanan zuwa gobe
insha allahu
Tace yauwa yayana dagananma akwai Maganar
da nakeson zamuyi
Yai murmushi yace kinsanni da qaguwa Akan son
Jin zance fara labaartamin naji
Aransa addu,a kawai yake Allah yasa cewa za(ai
tana sonsa
Tace a,aa yayaa saidai kaxo yace alqawari fa
tace eh nayi
Sukai sallama ya kashe wayar
Har ranta tannason bawan allahn yanada kyau
gashi da kyawawan dabi,u
Bayan sallar isha,i duk suna zaune a falon
daddyn nasu mommy da sauran yaran
Qannenta da afisa tana kusa da mommy tace
Shinema ko kiyi cigiyata tun yammah ko?
Mommyn ta kalleta da murmushi
Tace na leqa ai naga kina Barci daxun
Tace yauwa momy daxun mukai waya da danki
yace wai yana gaisheki wai gobe zaizo
Momyn tace yai zamansama aini nai fushi dashi
Nafisa ta dubi Momyn nata kamin ta maida
kallonta kan kausar din
Ke kuma meya hadaki dashi?a ina kika samu
lambarsa?
Tace ke kinjimu da anty dan bakison mutum saiki
hana Kowa mu,amala dashi
Nafisa tace uban wa ya gaya maki bana sonsa
iye?
Kausar ta dauke kanta daka kallonta tana kallon
daddy dake fadin
Ke meye haka bana hanaki wannan dabi,ar ta
zagi ba?
Ta shagwabe tace to daddy nifa sonsa nake haka
kawai
Sai taita shishshige masa
Yace waye?
Tadanyi murmushi kamain tace aleeyu mana
daddy danka
Wani irin fara!a ce a fuskarsa yace alhamd yata
Ba qaramin farinciki wannan abun yasaniba
Da kaina zan masa magana gobe daman dazu
yake fadamin ya kammala
Karatunsa kinga sai!a tsaida rana kawai
Ko kusa mommy bataso hadinba dan haka
fuskarta ko walwala babu
Tace amman kuwa Alhaji ya kamata a tuntubi
yaronnan aji
Tabakinsa dan hadinnan Kwata Kwata baiba
Dan halinsu ko kadan baixo dayaba inama laifin a
hadashi da kausar
Dan da itace kawai zasu iya samun kwanciyar
hankali
Nafisa kuwa ta raina Kowa bata ganin jama,a da
gashin arziqi
Ga girman kai
Alhajin yace ni nasan ba zamu samu matsala da
yaronba sannan ita kausar din ba sai in
tanasonsa ba
Kinsan ni bazanma Dana auren doleba tunda dai
ita nafin na sonsa
Sai muyi fatan alkhairi
Momy taace haba Alhaji ai baabu yarinyar da 
za,aa Bama aleeyu tace bai mataba
Dubi iyayi irin na nafisa amman tace tanasonsa
inaga kausar
Kawai saidai muce Allah ya zaba abinda yafi zana
alkhairi
Ya amsa da amin
Kausar ta dago da idanunta wadanda suka kada
Sukai jajir
Ta miqe jiki a sanyaye ta fice
Tuni tausayin yar tata ya kamata dan Tuni ta
Gano kausar Nason aleeeyun
Kuma Shima ta fahumci yana sonta
Saidai babu yaddah zasuyi da abinda aallah ya
hukunta
Lokacin da Alhaji muftahu ya tunkari aleeyu da
jancen
Ya rasa shi a wace duniya yake ba halin yaqi
aaamincewa dan
Bazai iya watsama uban Gidan nasa qasa a fuska
ba
Don haka ya amince
Da kansa alhajin yaaje qauyensu aleeyun ya
sanar dasu aauren ba qqaramin faarin ciki Sukai
ba aka tsaidaa ranar auren wataa mai kaamawa
Tunda akaa tsaaida maaganar auren aleeyu ya
gazaa zuwa gidaa Sbd tashin hankalin da yake
ciki
Ta yaya zai iya rayuwa babu kausar?
Alhajin daa kaansa yaima aaleeyu magaana
aakaan rashin zuwansaa zance yaji kunya sosai
dan haka ya tsaida ran Akan yau zaaije baaaayan
sallar isha,i
Yana gamaa sallr kuwaa yaaa wuce ba wata
kwallliyace a jikinsabaa
Tshirt ce kawaai baqaa da jeans
Yaasan shi mai laifine hakan yasa kai tsaye ya
nufi Cikin gidan
Yai sa,a kuwa duk suna falon gabaa daayaansu
Kai tsaye idonsaa kan kausaar yai
Zuciyaarsa ta tsinke daya lura shikenan sun
haramta ga juna kenan
Jinda yai ana fadar ah aleeyu ne yasa yai
Saurin dauke idanunsa yaa shiga yana nine momy
Suka gaisa sosai shida mommyn da daddyn
baayan sun Gama gaisawane
Daddyn yace ai saiki kaishe can falon baaqi ku
zantan ko Cikin zumudi tace taso muje tashi
kawai yai ya bita ba tare da yace komaiba
amman hankalinsa da
Tunaninsa nakan kausar Bayan sun fitane daddyn
yake cewa a wani sbn bank da za*a Bude
kwanannan na samar masa aiki. Zai zama
manajan bankin
Momyn tai murna sosai
A falon ya sameta ta saki wani irin murmushi
Tace yauwa nawan kokaifa idanunka sunfi komai
daukar hankali
Tadanyi shiru kamin tace nasan badaa son
raankaa ka kawomin wannan ziyarar ba
To amman ba yaddah zakai yaddah na ganka yau
haka nakeson ganinka gobe jibi
Kullunma ka gane ko?
Idan bakazoba to ni zanzo kuma ko gabansuwa
kake to
Saina baka kunya
Tunda na lura kai komima kunyarsa kakeji
Sannan idan daddy ya tambayeni ina zanje ko ina
naje nace masa kaika kirani kace naje na sameka
Kallonta kaawai yake dan Kwata Kwata baya
hayyacinsa
Dan haka yabarta tanata zuba kusan awa daya
sai surutu take ko qala baice mataba
Saima tashi da yai yace zai tafi ta riqeshi wai a
dole saiya qara jira
Saida yai da gaske ya samu ya zame ransa cike
da baqin ciki
Ba yaddah zaiyi dole yasama ransa sa,ida Allah
yasa hakan shiyafi zama ailkhairi
Ba yaddah ya iya haka ya dinga jera kwanaki
kullun sai yaxo
Ya samu aikinsa dan harya soma zuwa office
Sun bashi gida qato tsaraarre tare da wata mota
mai numfashi ta banki da miliyoyin kudi domin
wanke talauci
Momy tasa amarya tare da kausar Akan suje su
gaishe da iyayen aleeyun
Momy ta shirya musu tafia harda aleeyun da
tsaraba
Na kece raini
Direban Gidan ya daukesu a mota sai garin
musawa a jahar katsina unguwar saniyawa
Tunda suka hau hanyar qauyen naafisa ta dinga
waige waige
Can dai ta kasa daurewa ta dubeshi tace
Tace kai aleeyu wai yanxu mutanene ke rayuwa a
Cikin wannan dajin kauyen?
Tambayar tata ta bigi zuciyarsa tazo masa wuya
Yai wata murmushi da za* a iya kira da yaqe
yace
A wannan dajin kauyen da kika gani mahaifinki
yai rayuwa tun yana dan shekara sha biyar har
yakai ashirin
Tsit tai tankar ruwa ya cita amsar tai mataqar
yima kausar dadi
Dan ko banza yayi maganin iskancinta.
''Muhadu a chapter 4''


