AURE KAN AURE
Chapter 6
Bata amsa mataba ta shga cire kayan jikin nata
saida tai tsirara sannan
Ta juyo tana murmushu tace yadai kin shirya tai
Shru tana tunani bata angaraba sai ji tai suraiyar
ta janyota jikinta
Ta bita da kis a haka har tai nasaran cire komai
na jikin nata
Ta jata suka shga wani bangare wanda
Babu komai a wajenn sai nnamun daji tuni fitsari
ya soma bin qafata
Tuni cikinta ya murda lokacinda surayyah ta juyo
ta kalleta a lokacin
Zawon datake riqewa ya kece mata
Dan gaba daya haliTtarta ya sauya jikinta yai
wani haske Kamar wutan lantarki idanunta ya
zazzaro sunyi jajir
A take ta fasa wata uban ihu ta zube a wajen cak
ta dauketa tai
Ciki da ita
Mutanene a wajen dukkansu halittarsu ta koma
irinta
Sury sun kasu gida biyu. Gabas da kudu
Sunsa wani mutm mutumi a tsakiya
Gabansa wata qatuwar tukunyace daketa hayaqi
Sai Wasu surutai suke
Surayyah ta iso ya miko Mata hannu ta mika
masa nafin Sannan ta koma gefe inda sauran
jama,ar suke ta tsaya
Mutumin ya dinga zagayawa da nafin a bakin
tukunyar har sau uku
Sannan ya ajeta a tsakiyar filin
Ya koma inda tukunyar take yana Wasu yan
surutai Bayan ya gamane ya fara
Kwara Mata kira da karfinsa wata iska na fita
daga bakinsa
Naafisa Nafisa nafisa ta meqe a gigice tana waige
waige kafin ta runtse idanunta da qarfi
Ya barke da wata mahaukaciyar dariya kafin yace
maraba da zuwa nafi
Maraba da zuwa wannan gungiya tamu
Da farko muna miki barka da isowa
Na biyu kuma sharadinmune na uku kuma albishir
Sharadi kuwa shine duk Wanda yazo wannan
gungiya tofa baya fita har sai in baya numfashi
Inkuwa yace zai bijire mana to abu mai sauqi
shine zamu yankashi aljani yasha jininsa mu
kuma mu cinye namansa
Kuma duk abinda muke buqata saian kawo mana
ba,a yin mana gaddama
Inkuwa kai to haukataka zamuyi
Na uku shine albishir kin nemi duniya kin samu
Ba abinda zaki Nema indai kudi na siyansa a
duniya ki rasa dan
Haka muna miki maraba da shigowa kungiyar
@secret society
Hankalin Nafi ya soma kwanciya taja ajiyar
zuciya qarqarfa da taji ashe ba Ita za,a
Maida kudinba
Indai har Itace zata samu to aiko ko meye zaata
iya
Dan haka ta tashi tsam
Tana fadan na amince kungiya ta shaida nima na
zama yar gungiya abin yai
Musu dadi matuqa sukasa daria
Mutumin yace Nafi aljani na buqatar jininki
Ji tai hanjin cikinta na kadawa ta dinga matsawa
baya baya tana neman hanyar guduwa
Surayyah ta fito da wata yar qaramar wuqa ido
waje Nafi ke kallonta kafin tai wata
Wata harta capki tannunta ta yanki fatarta ta
tara wata yar qaramar kwarya
Bayan ta gama tsiyayan jinin ta saki hannun nata
taje ta miqama mutumin
Tace gashi sha jini sunan data kira mutumin
dashi kenan
Ya amsa gamida sa dogon harshensa ya shanye
jinin ya fasa kwaryar gamida fasa wani uban qara
yace kinxo hannunmu Nafi duk inda zaaki shiga a
tafin hannunmu kike
Baki isa ki layance manaba dan muna ganin
abinda ke cikin
Zuciyarki
Don haka wa kikafi so a wannan duniyar nafi?
Muryarta na rawa Sbd radadin yankar da
surayyah tai mata
Tace daddy na
Ya babbake da wata iriyar dariya kamin yace
Yace to muna buqatar jininsa kungiya na buqatar
namansa
Ta miqe tsaye a gigice tana fadar waye dadin
nawa?
Wanda yafi Kowa sona a duniya. Wanda yafi
riritani a cikin yayansa
Yafi sona da Kowa? Wanda ya haifeni yaci dani
ya shayar dani
Na tsawon wani shekaru ba tare da gajiyawa ba
Wanda yaban ilmin da kansa
Bazan iyaba inndai hakane na fita.........na
fita.......,afi.....''
Dariyar da yake kyalkyata mata Ita ta hanata
qarasawa
Da hannu ya nuna mutum na farko yace
Ba bada matata Ba biyu yace na yayata na bada
Na uku yace nahaifina na bada
Na hudu yace. Dana na cikina na bada
Na biyar yace nima mahaifiyata na bada
Akaxo kan surayyah tace mahaifina na fada da
kuma
Dana nasir Wanda shi kadai na haifa a duniya
Akaxo kanna takwas yace ni matata na bada na
tara
Tace ni mijina na bada
Akaxo kan na goma tace
Nakai shekara ashirin nida mijina ban taba
haihuwa ba Allah yaban ciki na haifi mace
kyakkyawa ran suna dodo yace yana buqata ba
yaddah
Na iya haka na miqata
Bayan sungamane akaxio kan uban gayyar sha
jini ya daka mata tsawa yace kin ganni nan
Uwata ubana matana dukkansu hudu yayyina
biyu qannena biyar yayana takwas
Uku maza biyar maza duk anan akai kwanjensu
dodo yasha jininsu gungiya taci namansu to dan
haka ko kinaso ko bakyaso ko kin shirya
Ko baki shiryaba. Tunda har kungiya ta buqaci
jinin mahaifinki tofa saikin kawoshi
Saidai zamu iya baki zabi ki zaba shin naki ran
kona mahaifinki?
Dan haka mun baki nanda kwana uku koki
kawoshi ko kuma dodo yasha jininki
Mu kuma muci namanki
Dan haka saiki zaba rayuwarki kota mahaifinki
Ya fashe da wata irin daria kafin bata ya bace
Kowa ya kama gabansa jikinta sai rawa yake sury
tai gaba har ta bita ta daga mata
Hannu ta nuna mata wata qofa tace na zatabi
Cikin tsananin tsoro tace Wlh bazan iya biba sury
Suryn ta dafata tace daurewa zakiyi ki runtse
idonki kibi inkuwa kikasa tsoro to hanyar wani
aljanin zakibi
Ya tsotse miji jini
Zakiga abubuwan ban tsoro da yawa ki nutsu in
kika tsorata to haukacewa zakiyi Ta saketa ta
nuna mata hanyar Ita kuma abi tata hanyar
Kuka nafin ta saka tace shin wane irin bala,i ne
ke tunkarota
Lol ni kaina na fara tausaya miki.
Muhadu a chapter 7......


