logo

HausaNovel: Aure Kan Aure Chapter 1



AURE KAN AURE
*Book1*
Chapter1*
Bugun qofar da ake tamkar za,a balle kyauren
shiya Tilastama Hajia nafisa tashi daga kishin
giden da take Tamkar wacce tasha wani uban aiki
ta gaji Tamkar wacce aka tunzura ta jira silifas
dinta dake gefen kujeran nata ta nufo qofar cikin
sauri Tana fadin dakata ku dakata Ta bude qofar
tana musu kallon Uku kwabo kamin taja wani
Dogon tsaki mtwwwww Kai bagidajen mutu baiba
a rayuwa inba gajidaje dan qauye ba Waye zaizo
yaita buga qofa yafi minti talatin ba,a budeba.
Kuma ya nace yaqi kama gabansa Ta kauce tace
ku shigo kar a koma qauye ace na hana yan uwa
shigowa gidan dan uwa Basuce da ita uffanba
saima da suka shige suka kama rawar jikin
gaisheta Ta daga musu hannu ku saurarar
Banason hayaniya kunji ko Kada ku cika mana
gida da warin baki tai gaba ba tare data basu
Izinin qarasowa ba Hakan bai hanasu damar
shiga falonba suna qoqarin zama kan kujera ta
daka musu tsawa Kai ku dakataa Karku sake
waye ya baku izinin zama kan kujera? Ku zube a
qasa duk wqacce ta zaunamin akan kujera wlh
sainaci mutuncinta Nina rasa irin wannan maita
sai kace ku kadai keda dan uwa Ku ala dole
dangin miji Ko wacce ta kwaso busassun
qafafuwanta babu ko wadatar basilin Dan a
ketamin yadin kujera da busassun. Fatar jikinku
ko To ku zube a qasa kuyita zama inya dawo dan uwan naku kwa ganshi Ta balbalesu da harara
Tana fadin munafukai inda bashi Dashi babu mai
kallonsa balle ya taimaka masa da ko sisi Tai
tsaki ta juya ta haye saman benenta Tun misalin
qarfe hudu na yamma suke tule babu wanda ya
waiwayesu Saidai masi aikin gidan wata budurwa
da tsohuwa daketa kaiwa da komowa Akai sallar
magrib duk sunanan Zube soma suke a nuna
musu toilet dan su dauro alwala Suyi sallah
amman da sukaima yan aikin magana sai sukace
wai hajia bata basu iziniba Sunanan zaune har
akai sallar isha,I yar yarinyar waddah Bata wuce
shekaru27 ba ta dubi dattijuwar waddah ba zata
gaza Shekaru hamsinba Tace goggo kodai ki tashi
muje gida kawai Dubi yaddah aka watsar damu
sai kace bola anan Yar tsohuwar da ake kira da
gwaggo tace Ke tashi nan wawiya in zamu
kwanan anan munanan a zaune har sai yaxo In
har muka ganshi sakarya mun warke Ta gyada
kai to allah e kawoshi lfy Qarfe tara daidai aliyu
ya shigo gidan nasa yana shigowa yai ido hudu
da yan uwan nasa Da sauri ya qarasa yana Ah
gwaggo yaushe kukaxo? Tafiyar dare kukai? Ya
duqa gwiwa bibbiyu yana gaisheta ta amsa da
fara,arta Dajin dadi rakiya ma ta gaidashi Ya
amsa yana maimaita tambayar tashi yanxu
kukaxone Kokun biya wani kurin? Gwaggo ta tabe baki tace ba inda muka biya ali gidanka muka
Yoma tsinke Wannan yar iskar matar taka marar
mutuncin ita ta zubar damu tun la,asar muke Nan
zube Kaidai bakai sa,ar mataba wlh Bakai sa,ar
maceba ali Cikin rashin jin dadi yace kuyi haquri
dan allah gwaggo Ya miqe da sauri sashin masu
aiki ya nufa yana kwalama ladidi Kira Tazo ta
zube a gabansa tace gani Yace anbama baqinda
sukaxo abinci kuwa? Cikin rawar murya tace ai
hajia Bataceba Ya dafe kai cike da takaici Ya
dago ya dubeta Yace jeki kai musu abinci sannan
Ki hada musu da lemukan kwali da juice kikai
musu Kuma daga yau duk wanda ya shigo cikin
gidannan kar,a sake a barshi ya fita har sai an
bashi abinci yaci ya qoshi saidai idan shine yace
bazai ciba Jiki na rawa tace an gama ranka ya
dade Sannan ya juya ya fita ya koma wajen
goggon tasa e zauna yana Fadar Amman ba
ganki da ruqayyah goggo ina mijin nata? Cike da
takaici tace ai kasan irin halin naku na maza ali,
Kishiya jibro yai mata kuma ya soma wulaqantata
dan yayi amarya Shine tayi yaji Kagantanan yau
kwananta uku Da mijin ya biyo sahu nai masa
Tatas Naja masa kunne nace Kuma gobe zan
koma da ita da kaina To kasan halin naku indai
mace Bata da wani dan sana,a bata maida taro
ya zama sisi Shikenan kun rainata kenan Shine
nazo Na rokeka ka siya mata wani dan abun da zata dinga sana,a Dashi acan qauyen don allah
Ya gyara zama yana ai wannan Ba wani abu bane
Goggo Ya dubi rakiya yana fadar ke yanxu Me
kikeso a siyan miki Wanda kikasan yanada saurin
Kawo kudi? Tace duk abinda ka siyamin yayi
Goggo tace ni nasan abinda za,afi samun kudi
dashi Ka siya mata injin murjin taliya Da keken
dinki tunda ta iya Dinki tun tana gida Yace to
shikenan goggo allah Ya kaimu goben insha
allahu Zansa a siyo mata Nan suka shiga godia
ladidi ta shigo musu da kwandon abinci Ta jejjera
musu da flate Cokula da kayan drinks yace ladidi
Jeki kyara musu dakin baqi idan sun gama sai ki
nuna musu dan suje su huta Ta amsa da to Yace
shikenan goggo koda akwai Abinda kuke buqata?
Tace ba komai goggo allah yai Maika albarka ya
kuma sauya maka da mata ta gari Baice komaiba
murmushi kawai Yayi ya miqe ya nufi sama S
saman benen sashi biyu ne Hagu da dama.
Dauke da katafaren falo Wanda aka qawata da
manyan kujeru da kayan alatu Zamu iya kiran
wannan bangare da aljannar duniya A cikin falon
akwa bedroom biyu wanda yake dauke da
qaramin Toilet Duk abinda yake wannan sashin
akwaishi a dayan sashin Hatta capet din dake
tsakiyar dakin Sashin matarsa ya nufa ya kashe
kayan kallon daketa ruri Banza ya nufi bangaren
nata Kwance take saman katafaren gadonta dake
dauke da kayan alatu Daga ita sai wata
gajeruwar rigar bacce Iya cinya mai sulbi Gashin
kannan a barbaje saman Filo Tai rub da ciki
tanata latse latse A. Laptop dinta Yana sallama ta tashi ta zauna Bakinta dake da murmushi
Wooo welcome my one Babu alamar zai mayar
mata da murmushin fuska ya qara daurewa Ya
jingina da bango ya harde hannayensa a jikin
kirjinsa Yana kallonta Tadai? Ta fada tana
kallonsa ba tare data qara matsawa daga inda
takeba Fuskar tashi ba walwala ya soma magana
Nafisa wulaqancin da kikemin ya soma isata cin
fuskar da kikemin ya isa haka Ki sani yanda
kikeson danginki yan uwanki da iyayenki haka
nima nakeson nawa dangin Yan uwana da
iyayena Ya taka har gabanta yana nunata da
dogon dan yatsansa Yana fadar Na rantse miki
da girman allah Ki kiyayi wulaqantamin yan uwa
ya isheki haka Wani murmushi taja hade da tabe
baki tana fadar Sannu mai iyaye dan allah kai
bakaji kunya ba? Ka dubi wadannan damejin
halittun har kake kiransu da yan uwanka.?
Kauyawa gidadawa wadanda kircin talauci ya
ishesu'' Ji yayi tamkar tana watsa mishi Garwashi
a kirjinsa Ya daga hannu zai watsa mata mari
Tunanin me yayi kuma sai ya fasa ya sake
hannun nasa Idanunsa sunyi jajir Ya juya a zafafe
yabar dakin Nata zuciyarsa na tafarfasa Kamar
garwashin wuta Shi nafisa take zagi? Yanxu ta
Zage masa tushensa asalinsa iyayensa? Ya
damqi sumar kansa yaja da qarfi Idanuwannan
suka rikice tamkar Jan gauta Shin wacce
qaddarace ta hadashi Da nafisa? Mai yasa yai
auren Kudi? Meya kaishi auren macen data
Kerema ajinsa? Kuma iyayenta suke taqama da
yayan banki? Mai yasa bai tsaya inda allah ya
ajeshiba ya auri tushensa irin asalinsa? Da yanxu
bai samu kansa a wannan baqin cikin da
takaicinba Ya ilahi Abinda ya fada kenan Ya fada
saman kujeran dake falonsa Zuciyarsa naci gaba
da tafarfasa Tamkar wanda aka tsikara ya miqe
da sauri yai hanyar fridge Ya bude ya dauko
roban ruwan faro ya murda ya dinga zazzagama
cikinsa Ya dire robar saman fridge din da qarfi Ya
koma ya kishin gida sanyin ruwan na ratsa mashi
zuciya Tunanin abinda suka faru shekarun da
suka wuce suka dinga dawo masa Shin meye ya
faru a shekarun Baya saiku biyoni danjin ko
wadanne abubuwane suka faru-------

Kubiyomu Domin Karashen Labarin 'Aure Kan Aure......

Tags

advertisement centil

This blog is created for your interest and in our interest as well as a website and social media sharing info Interest and Other Entertainment.